text
stringlengths
1
6.82k
dangantaka tsakanin kasashen masar da turkiya ta yi tsami a cikin yan kwanakin nan saboda sanin iyakokin da kowanne daga cikin yake mallaka a tekun mediterranean
kamfanin dillancin labaran irna na kasar iran ya nakalto ahmad abuzaid kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar masar yarjejeniyar da kasar masar ta cimma da kasar cyprus kan iyakokin da kowanne daga cikinsu yake mallaka daga gabacin tekun mediterranean ta zama doka ce kuma duk wanda yayi kokarin taka ta masar zata kalubalance shi
abuzaid ya kara da cewa yarjejeniyar rabon kan iyaka a cikin tekun mediterranean yarjejjeniya ce ta kasa da kasa wacce majalisar dinkin duniya ta amince da ita
amma ministan harkokin wajen kasar turkiya maulud chavisuglu a ranar litinin da ta gabata ce ya bada sanarwan cewa kasar turkiya ba ta amince da yarjejeniyar da kasashen masar ta cyprus suka cimma kan rabon kan iyaka da kuma amfani da tekun mediterranean a shekara ta 2013 ba
wani sabon sabani ya kunno kai tsakanin kasashen masar da turkiyya
masar ta zargi mahukuntan turkiyya da kokarin yin zagon kasa ga harkar tattalin arzikin kasarta
yesu ya zabi manzanni goma sha biyu _ darussan littafi mai tsarki don yara
yesu ya zabi manzanni goma sha biyu
yesu yana da wata shawara mai muhimmanci da yake so ya yanke bayan ya yi shekara ɗaya da rabi yana waazi su wane ne zai zaɓa su yi aiki tare da shi su wane ne zai horar da su don su jagoranci ikilisiyar kirista yana bukatar taimakon jehobah don ya yanke wannan shawarar don haka ya tafi kan dutse inda babu kowa kuma ya yi dukan dare yana addua da safe sai yesu ya kira wasu mabiyansa kuma ya zaɓi manzanni guda 12 shin ka tuna sunayensu sunayensu bitrus da andarawus da yaƙub da yohanna da filibus da bartalamawus da toma da matta da yaƙub ɗan halfa da taddawus da siman da kuma yahuda iskariyoti
manzanninsa goma sha biyu za su riƙa tafiya da shi bayan ya horar da su sai ya tura su yin waazi jehobah ya ba su ikon da za su iya fitar da aljannu da kuma warkar da marasa lafiya
yesu ya amince da manzannin sha biyu kuma ya kira su abokansa farisawa suna ganin cewa manzannin ba su da ilimi kuma su talakawa ne amma yesu ya horar da su don aikin da za su yi za su kasance tare da yesu a lokuta mafi muhimmanci a rayuwarsa wato kafin ya mutu da kuma bayan an tayar da shi daga matattu kamar yesu yawancin manzannin sha biyu daga galili suke wasu cikinsu maaurata ne
manzannin ajizai ne kuma sukan yi kuskure a wasu lokuta sukan yi magana da garaje kuma sukan yanke shawarar da ba ta dace ba suna fushi a wasu lokuta sun ma yi musu a kan wane ne a cikinsu ya fi girma amma su mutanen kirki ne da suke ƙaunar jehobah su ne za su kula da ikilisiyar kirista bayan yesu ya koma sama
na ce da ku abokai gama dukan abin da na ji daga wurin ubana na sanar muku da su​yohanna 1515
tambayoyi su wane ne yesu ya zaɓa su zama manzanninsa 12 mene ne yesu ya aiki manzanninsa su yi
darussa na daga littafi mai tsarki
ku taimaka wa yaronku ya koyi sunayen manzannin 12
gfi languard shine babban masanin kimiyya na tsaro na cibiyar sadarwar da kuma magance matsalar gudanarwa wanda ke aiki a matsayin mai kula da tsaro mai tsaro yana ba ku cikakkiyar hoto na saitin cibiyar sadarwa yana samar da bincike mai hadarin gaske kuma yana taimaka maka ka ci gaba da hanyar sadarwar da ke da tabbaci tare da ƙoƙarin ƙananan gfi languard zai gano sabobinka ɗawainiya kwamfyutocin kwamfyuta na'urorin hannu irin su wayoyin hannu da allunan har ma da inji mai mahimmanci masu sauyawa da mawallafi yin amfani da dashboard don nazarin sakamakon binciken a gefen hagu za ka iya ganin kwakwalwa a cibiyar sadarwa da wayoyin hannu da kuma allunan da ke haɗi zuwa asusunka na microsoft exchange
module kulawa na ayyukan 9
sau nawa mutanen da ke dauke da cutar sida na gwaji help center
mutanen da ke dauke da cutar sida kan fara gwaji da zara sun fara shan magani daga wurin mai kiwon lafiya sannan sai ya tsara masu gwajegwaje na gaba
da zarar mutum ba shi da tabbas na tsawon watanni shida an bada shawara cewa ya je gwajin kowane watanni shida
domin karin bayani a duba hivgov (wurin dubawa da turanci)
ghana ta hana kamun kifi a fadin kasar _ labarai _ dw _ 07022017
ghana ta hana kamun kifi a fadin kasar
kimanin kashi 10 cikin dari na al'ummar ghana sun dogara ne ga kamun kifi a harkokin su na rayuwar yau da kullum
ggwamnatin ta ce kifayen na iya karewa idan ba'a dauki matakin hana yin su din musamman a manyan kogunan kasar ba
sai dai kuma masu harkar sana'ar kifin sun ce matakin bai yi musu dadi ba a cewar naa quartey wata mai sanar kifin
za mu je mu zauna a gida a na tsawon watanni biyu babu shakka wannan zai shafi rayuwar mu kowa na juyayin wannan al'amari musamman na'urar sanyi da muke haya domin zuba kifi ko ka ajiye kifi ko baka ajiye ba sai ka biya a saboda haka wannan hasara ce a gare mu
a baya bayan nan dai masunta a kasar ta ghana sun koka cewa basa samun kifi sosai duk da tsawon lokaci da suke dauka bayan shimfuda fatsa a kogi lamarin da aka dora alhakinsa akan hanyoyi mara sa inganci na kamun kifin wanda baya barin ko da 'ya'yan kifayen ne
muhimman kalmomi ghana kamun kifi sana'ar su
shugaban kenya ya samu sabon wa′adi _ labarai _ dw _ 12082017
shugaban kenya ya samu sabon wa'adi
hukumar zaben kenya ta tabbatar da cewa shugaba uhuru kenyatta ya sake lashe zaben shugaban kasa
an samu zangazanga da tashetashe hankula a wasu sassan kasar kenya yayin da a wasu sassan mutane suka sheke da murna bayan hukumar zaben kasar ta kenya ta tabbatar da shugaba uhuru kenyatta a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar a karo na biyu
shugaban hukumar zaben kasar wafula chebukati ya bayar da sanarwar inda shugaba kenyatta ya samu nasara da lashe kashi 54 cikin 100 na kuri'un da aka kada yayin da jagoran 'yan adawa raila odinga ya samu kashi 44 cikin 100 na kuri'un an dai jibge daruruwan 'yan sanda a birnin nairobi fadar gwamnatin kasar domin tabbatar da doka da oda yayin da magoyan bayan jagoran 'yan adawa raila odinga ke nuna rashin yarda da sakamakon shi kansa shugaba uhuru kenyatta dan shekaru 55 ya yi kan hakin kan kasa tare da neman 'yan adawa su yi aiki tare
shugaban na faransa ya ce zai zamo kakakin kasashen biyar wajen nemo kudaden gudanar da ayyukan rundunar sai dai kuma macron ya ce sai sojoji da za a dauka cikin wannan runduna sun yi abun azo a gani tare da gamsar da kasashe cewa rundunar ka iya zama madogara a yakin da ake da 'yan jihadi
ya ce wadannan hareharen 'yan ta'adda na kara mana kuzarin hada karfi da karfe domin yakar ayyukan ta'addanci ga baki dayansa a kullu yaumin muna fama da 'yan ta'adda ko wasu malatata da ta kamata mu manta da sunayansu da ma fuskokinsu mu daukesu kawai abokan gaba da ta kamata mu ga bayansu
rahotanni daga chadi na cewar wasu harehare bam da aka kai sun yi sanadin rasuwar mutane akwalla 27 a wata kasuwa da ke tsibirin loulou fou
shaidun gani da ido sun bayyanawa kamfanin dillancin labarai na ap cewar baya ga wanda suka rasu din wasu da suka kai 90 sun samu raunuka wasunsu ma munana
mai magana da yawun rundunar 'yan sanda chadi din a wajen da wannan hari ya wakana ya ce wasu mata ne uku dauke da bamabamai suka kai harin
ya zuwa yanzu dai babu wata kungiya da ta dau alhakin kai wannan harin sai dai kungiyar nan ta boko haram ta kai jerin harehare a chadi din don ko a watan jiya ma sai da wata 'yar kunar bakin wake ta hallaka mutane 3 a wani kauye dab da tafkin chadi
muhimman kalmomi chadi boko haram harin kunar bakin wake
ma'aikatar shari'a ta kasar chadi
tun dai a ranar 13 ga wannan wata na janairu aka kafa kwamiti a wani mataki na fadada bukatar neman a sallamo dan fafutikar daga tsaron da ake yi masa tun daga tsakiyar watan satumba na 2016 sakamakon wasu kalamai da ya yi na suka ta shafinsa na facebook ga shugaban kasar ta chadi idriss deby itno a cewar mai magana da yawun kwamitin da aka kafa jeanbosco manga yanzu dai sun shigar da kara domin ganin an sake shi
a cewar kungiyar kare hakin biladama ta amnesty international an dauke dan fafutikar tadjeddine mahamat babouri yayin da yake tafiya a tsakiyar titin birnin n'djamena 'yan kwanaki kalilan bayan da ya wallafa wani bidio na sukar shugaba deby inda ake ci gaba da tsare shi a gidan kaso na moussoro da ke tsakiyar kasar bayan da ya shafe watanni da dama a gidan kaso na koro toro da ke arewacin kasar
kai ne a nan gida / archives ga ƙara matsaloli / abin da don ci gaba
me kake son girma
wani irin hatsi kuke sha'awar
shuka kome sai dai hatsi da kayan marmari
wani irin kayan lambu kake sha'awar
fiye da mutane miliyan 6 na fuskantar tsananin yunwa a sahel mdd afrika rfi
fiye da mutane miliyan 6 na fuskantar tsananin yunwa a sahel mdd
wasu daga cikin yara masu fama da karancin abinci a yankin sahel wikipedia
shugaban hukumar jinkai ta majalisar dinkin duniya mark lowcock ya yi gargadin cewar ana fuskantar matsalar samar da abinci a yankin sahel wanda ke nuna karuwar mutanen da ke fuskantar matsalar abinci mai gina jiki irin sa na farko tun bayan shekarar 2012
jamiin ya ce akalla kusan mutane milyan 6 ne ke shan wahala wajen samawa kan su abinda za su ci a kasashen burkina faso da chadi da mali da mauritania da nijar da kuma senegal inda yara sama da milyan guda da rabi ke fama da tamowa
lowcock ya ce yanzu haka milyoyin mutane sun cinye dan abincin da suka yi tanadi yayin da wasu suka fara rage yawan abincin da suke ci a rana da kuma janye yaran su daga makarantu
jamiin ya kuma ce matsalar rashin abincin ya karu da kashi 50 yayin da kowanne yaro guda daga yara 6 ke bukatar kulawa ta musamman
kasashen duniya za su tallafawa g5
taron taimaka wa rundunar tsaron
shugabannin yankin sahel 5 na taro kan
shafin yada labarai na lu'alua ya abyar da rahoton cewa a yau ne iyalan babban malamin addinin muslunci na kasar bahrain ayatollah isa qasim suka dauke zuwa asibiti sakamakon matsalolin ciwon suga da hawan jini mai tsanani da yake fama da su
mahukuntana masarautar kama karya ta kasar bahrain sun bayar da dama ga iyalan malamin da su dauke shi zuwa asibiti a yau bayan tsare shi cikin gida na tswon lokaci tare da hana shi ganawa da jama'a
al'ummomin kasar bahrain da ma kungiyoyin kare hakkin bil adama na duniya sun gargadi mahukuntan masarautar kama karya ta bahrain dangane da makomar malamin sakamakon hana kai shi asibiti domin duba lafiyarsa wanda hakan yasa ala tilasta masarautar ta bayar da dama daukar malamin zuwa asibiti
masarautar kama karya ta bahrain ta killace gidan shehin malamin ne sakamakon kiran da yake ga mahukuntan kasar kan su baiwa kowane dan kasa hakkinsa amatsayinsa na dan kasa ba tare da tauye hakkin wani bangare ba
an kalubalanci obasanjo ya fito ayi muhawara da shi a talabijin kan wasikarsa daily nigerian hausa
home labarai an kalubalanci obasanjo ya fito ayi muhawara da shi a talabijin kan
an kalubalanci obasanjo ya fito ayi muhawara da shi a talabijin kan wasikarsa
wani fitaccen dan jarida mohamme garba ya kalubalanci tsohon shugaban kasa obasanjo kan ya fito ayi muhawara da shi a talabijin kan wasikar da ya aikewa shugaba buhari inda yake bashi shawara kan kada ya tsaya zabe a 2019
mohammaed garba wanda shi ne shugaban kamfanin right cantact servises ltd ya bayyana hakan ne a kaduna inda ya kalubalanci wasikar ta obasanjo yace a zamanin demokaradiyya wannan wasika bata wuce shifcin gizo ba
a cewarsababu wani dan najeriya duk girmansa da yake da yancin hana wani mahaluki yin takara a kowanne irin mukami kuma ko waye shi yancin duk dan kasa ne ya fito ya tsaya zabe ko a zabe shi
daga nan ya bukaci tsohon shugaban kasa obasanjo da ya bayyana dalilan da ya dogara a garesu daga kundin tsarin mulki da zai sanya ya hana wani mutum kamar shugaba mai ci sayawa takara
mohammed garba yace zai dauki nauyin tattaunawar a duk gidan talabijin din da obasanjon ya zaba daga nan sai yan najeriya su yiwa obasanjo tambayoyi kai tsaye na abinda yake nufi
abu ne a bayyane cewar akwai matsin lamba daga kasashen waje wadan da basa jin dadin yadda shugaba buhari ke tafiyar da alamura a najeriya da ma wasu miyagun yan siyasa na cikin gida da basa yiwa najeriya fatan alheri
ina da fahimtar cewar wasu marasa kaunar najeriya ne suke son yin amfani da obasanjo domin kawowa zaben 2019 matsala domin bakincikin arzikin da allah ya huwacewa kasar
ni mohammed garba a matsayina na kwararren dan jarida ina kalubalantar tsohon shugaban kasa da ya fito muyi wannan muhawara kan wannan wasika da ya rubutawa shugaba buhari
babu matsala tattare da tawagar ingila a rasha mourinho wasanni rfi
wasanni kwallon kafa ingila rasha gasar cin kofin duniya
babu matsala tattare da tawagar ingila a rasha mourinho
mourinho wanda ya bayyana kasashen brazil da jamus a matsayin wadanda suka fi hada tawaga mai kyau amma y ace tawaga mai kyau ba ita ke nuna cewa dole su za su yi nasara ba reuters/robert pratta
kociyan manchester united jose maourinho ya ce yana da yakinin cewa tawagar ingila da ta tafi rasha za ta kai labari a ilahirin wasannin da za ta dokakalaman mourinho na zuwa ne a dai dai lokacin da jitajita ke kara yawaita game da rashin gogewar tawagar da ingila ta tura rasha
akwai fargabar cewa hukumar kwallon kafar ta ingila ta yi ragon azanci wajen aikewa da kananan yara zuwa rashan wadanda galibinsu basu da gogewar irin gasar hasalima dai dai kune suka taba doka gasar cin kofin duniya
sai dai mourinho ya ce duk da cewa yara aka tura amma dukkaninsu suna da gogewar da ake bukata don kuwa kowannensu na taka leda a manyan kungiyoyin kwallon kafa dabandaban dama na firimiyar ingila
mourinho wanda ya bayyana kasashen brazil da jamus a matsayin wadanda suka fi hada tawaga mai kyau amma y ace tawaga mai kyau ba ita ke nuna cewa dole su za su yi nasara ba
ingila wadda ke a rukunin g za ta fara karawa ne da tunisia idan ta yi nasara kuma ta kara da guda cikin belgium ko kuma panama
salah ya lashe kyautar gwarzon dan
manyan kloblikan ingila da za su kai

No dataset card yet

New: Create and edit this dataset card directly on the website!

Contribute a Dataset Card
Downloads last month
146
Add dataset card