0
stringlengths
3
620
1
stringlengths
4
423
I will bless those who bless you and curse those who treat you with contempt. All the families on earth will be blessed through you.”
Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
So Abram departed as the Lord had instructed, and Lot went with him. Abram was seventy-five years old when he left Haran.
Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
He took his wife, Sarai, his nephew Lot, and all his wealth—his livestock and all the people he had taken into his household at Haran—and headed for the land of Canaan. When they arrived in Canaan,
Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
Abram traveled through the land as far as Shechem. There he set up camp beside the oak of Moreh. At that time, the area was inhabited by Canaanites.
Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
Then the Lord appeared to Abram and said, “I will give this land to your descendants. ” And Abram built an altar there and dedicated it to the Lord , who had appeared to him.
Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji , wanda ya bayyana gare shi.
After that, Abram traveled south and set up camp in the hill country, with Bethel to the west and Ai to the east. There he built another altar and dedicated it to the Lord , and he worshiped the Lord .
Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji .
Then Abram continued traveling south by stages toward the Negev.
Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
At that time a severe famine struck the land of Canaan, forcing Abram to go down to Egypt, where he lived as a foreigner.
To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
As he was approaching the border of Egypt, Abram said to his wife, Sarai, “Look, you are a very beautiful woman.
Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
When the Egyptians see you, they will say, ‘This is his wife. Let’s kill him; then we can have her!’
Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
So please tell them you are my sister. Then they will spare my life and treat me well because of their interest in you.”
Saboda haka ki ce ke ’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
And sure enough, when Abram arrived in Egypt, everyone noticed Sarai’s beauty.
Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
When the palace officials saw her, they sang her praises to Pharaoh, their king, and Sarai was taken into his palace.
Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
Then Pharaoh gave Abram many gifts because of her—sheep, goats, cattle, male and female donkeys, male and female servants, and camels.
Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
But the Lord sent terrible plagues upon Pharaoh and his household because of Sarai, Abram’s wife.
Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
So Pharaoh summoned Abram and accused him sharply. “What have you done to me?” he demanded. “Why didn’t you tell me she was your wife?
Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
Why did you say, ‘She is my sister,’ and allow me to take her as my wife? Now then, here is your wife. Take her and get out of here!”
Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita ’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
Pharaoh ordered some of his men to escort them, and he sent Abram out of the country, along with his wife and all his possessions.
Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.
So Abram left Egypt and traveled north into the Negev, along with his wife and Lot and all that they owned.
Saboda haka Abram ya haura daga Masar zuwa Negeb tare da matarsa, da dukan abin da yake da shi tare da Lot.
(Abram was very rich in livestock, silver, and gold.)
Abram ya azurta ƙwarai da dabbobi, da azurfa, da kuma zinariya.
From the Negev, they continued traveling by stages toward Bethel, and they pitched their tents between Bethel and Ai, where they had camped before.
Daga Negeb, ya ci gaba da tafiyarsa a wurare dabam-dabam har ya kai tsakanin Betel da Ai, a inda dā ya kafa tentinsa na fari
This was the same place where Abram had built the altar, and there he worshiped the Lord again.
da kuma inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji .
Lot, who was traveling with Abram, had also become very wealthy with flocks of sheep and goats, herds of cattle, and many tents.
Lot wanda yake tafiya tare da Abram, shi ma yana da garken shanu da tumaki da kuma tentuna.
But the land could not support both Abram and Lot with all their flocks and herds living so close together.
Wannan ya sa har ƙasar ba tă ishe su yayinda suke zama tare ba, saboda mallakarsu ta yi yawa har ba za su iya zama tare ba.
So disputes broke out between the herdsmen of Abram and Lot. (At that time Canaanites and Perizzites were also living in the land.)
Rikici kuma ya tashi tsakanin masu kiwon dabbobin Abram da na Lot. Mazaunan ƙasar, a lokacin kuwa Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.
Finally Abram said to Lot, “Let’s not allow this conflict to come between us or our herdsmen. After all, we are close relatives!
Saboda haka Abram ya ce wa Lot, “Kada mu bar rikici yă shiga tsakaninmu, ko kuma tsakanin masu kiwon dabbobinka da nawa, gama mu ’yan’uwa ne.
The whole countryside is open to you. Take your choice of any section of the land you want, and we will separate. If you want the land to the left, then I’ll take the land on the right. If you prefer the land on the right, then I’ll go to the left.”
Ba ga dukan ƙasar tana gabanka ba? Bari mu rabu. In ka yi hagu sai ni in yi dama. In ka yi dama, sai ni in yi hagu.”
Lot took a long look at the fertile plains of the Jordan Valley in the direction of Zoar. The whole area was well watered everywhere, like the garden of the Lord or the beautiful land of Egypt. (This was before the Lord destroyed Sodom and Gomorrah.)
Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji , kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
Lot chose for himself the whole Jordan Valley to the east of them. He went there with his flocks and servants and parted company with his uncle Abram.
Saboda haka sai Lot ya zaɓar wa kansa dukan kwarin Urdun, ya tashi ya nufi wajen gabas. Haka fa suka rabu da juna.
So Abram settled in the land of Canaan, and Lot moved his tents to a place near Sodom and settled among the cities of the plain.
Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, yayinda Lot ya zauna cikin biranen kwari, ya kafa tentunansa kusa da Sodom.
But the people of this area were extremely wicked and constantly sinned against the Lord .
Mutanen Sodom kuwa mugaye ne, sun aikata zunubi ƙwarai ga Ubangiji .
After Lot had gone, the Lord said to Abram, “Look as far as you can see in every direction—north and south, east and west.
Bayan Lot ya rabu da Abram, sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ɗaga idanunka daga inda kake, ka dubi arewa da kudu, gabas da yamma.
I am giving all this land, as far as you can see, to you and your descendants as a permanent possession.
Dukan ƙasar da kake gani zan ba ka, kai da zuriyarka har abada.
And I will give you so many descendants that, like the dust of the earth, they cannot be counted!
Zan sa zuriyarka tă yi yawa kamar ƙurar ƙasa, har in wani yana iya ƙidaya ƙurar, to, za a iya ƙidaya zuriyarka.
Go and walk through the land in every direction, for I am giving it to you.”
Tafi, ka ratsa tsawo da fāɗin ƙasar, gama zan ba ka ita.”
So Abram moved his camp to Hebron and settled near the oak grove belonging to Mamre. There he built another altar to the Lord .
Saboda haka Abram ya cire tentunansa, ya zo ya zauna kusa da manyan itatuwan Mamre a Hebron, inda ya gina bagade ga Ubangiji .
About this time war broke out in the region. King Amraphel of Babylonia, King Arioch of Ellasar, King Kedorlaomer of Elam, and King Tidal of Goiim
A zamanin Amrafel sarkin Shinar, shi da Ariyok sarkin Ellasar, Kedorlayomer sarkin Elam, da kuma Tidal sarkin Goyim
fought against King Bera of Sodom, King Birsha of Gomorrah, King Shinab of Admah, King Shemeber of Zeboiim, and the king of Bela (also called Zoar).
suka tafi don su yaƙi Bera sarkin Sodom, Birsha sarkin Gomorra, Shinab sarkin Adma, Shemeber sarkin Zeboyim, da kuma sarkin Bela (wato, Zowar).
This second group of kings joined forces in Siddim Valley (that is, the valley of the Dead Sea ).
Dukan waɗannan sarakuna na bayan nan suka haɗa kai a Kwarin Siddim (Teku Gishiri).
For twelve years they had been subject to King Kedorlaomer, but in the thirteenth year they rebelled against him.
Shekara goma sha biyu suna bauta wa Kedorlayomer, amma a shekara ta sha uku sai suka yi tawaye.
One year later Kedorlaomer and his allies arrived and defeated the Rephaites at Ashteroth-karnaim, the Zuzites at Ham, the Emites at Shaveh-kiriathaim,
A shekara ta goma sha huɗu, Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi suka tafi suka cinye Refahiyawa a Ashterot Karnayim, Zuziyawa a Ham, Emawa a Shabe Kiriyatayim,
and the Horites at Mount Seir, as far as El-paran at the edge of the wilderness.
da Horiyawa a ƙasar tudun Seyir har zuwa El Faran kusa da hamada.
Then they turned back and came to En-mishpat (now called Kadesh) and conquered all the territory of the Amalekites, and also the Amorites living in Hazazon-tamar.
Sa’an nan suka juya suka tafi En Mishfat (wato, Kadesh), suka cinye dukan ƙasar Amalekawa, da kuma Amoriyawa waɗanda suke zaune a Hazazon Tamar.
Then the rebel kings of Sodom, Gomorrah, Admah, Zeboiim, and Bela (also called Zoar) prepared for battle in the valley of the Dead Sea.
Sai sarkin Sodom, sarkin Gomorra, sarkin Adma, sarkin Zeboyim da sarkin Bela (wato, Zowar), suka fita suka ja dāgā a Kwarin Siddim
They fought against King Kedorlaomer of Elam, King Tidal of Goiim, King Amraphel of Babylonia, and King Arioch of Ellasar—four kings against five.
gāba da Kedorlayomer sarkin Elam, Tidal sarkin Goyim, Amrafel sarkin Shinar da Ariyok sarkin Ellasar; sarakuna huɗu gāba da biyar.
As it happened, the valley of the Dead Sea was filled with tar pits. And as the army of the kings of Sodom and Gomorrah fled, some fell into the tar pits, while the rest escaped into the mountains.
Kwarin Siddim kuwa ya cika da ramummukan kwalta, sa’ad da sarakunan Sodom da Gomorra suka gudu kuwa, waɗansu mutane suka fāɗa cikin ramummukan kwaltan, sauran kuwa suka gudu zuwa tuddai.
The victorious invaders then plundered Sodom and Gomorrah and headed for home, taking with them all the spoils of war and the food supplies.
Sarakunan nan huɗu suka washe dukan kayayyakin Sodom da Gomorra, da kuma dukan abincinsu, sa’an nan suka tafi.
They also captured Lot—Abram’s nephew who lived in Sodom—and carried off everything he owned.
Suka kuma kama Lot ɗan ɗan’uwan Abram, wanda yake zaune a Sodom, da kayayyakinsa, suka yi tafiyarsu.
But one of Lot’s men escaped and reported everything to Abram the Hebrew, who was living near the oak grove belonging to Mamre the Amorite. Mamre and his relatives, Eshcol and Aner, were Abram’s allies.
Sai wani wanda ya tsira, ya zo ya faɗa wa Abram mutumin Ibraniyawa. Abram kuwa yana zama kusa da manyan itatuwan Mamre, Mamre mutumin Amoriyawa ne ɗan’uwan Eshkol da Aner, su kuwa abokan Abram ne.
When Abram heard that his nephew Lot had been captured, he mobilized the 318 trained men who had been born into his household. Then he pursued Kedorlaomer’s army until he caught up with them at Dan.
Da Abram ya ji cewa an kama danginsa, sai ya tara horarrun mutane 318, da aka haifa a gidansa, ya bi sawun sarakunan da suka tafi da Lot, har Dan.
There he divided his men and attacked during the night. Kedorlaomer’s army fled, but Abram chased them as far as Hobah, north of Damascus.
Da dad dare, Abram ya rarraba mutanensa don su fāɗa wa sarakunan nan, ya ɗibge su, ya kore su har zuwa Hoba, arewa da Damaskus.
Abram recovered all the goods that had been taken, and he brought back his nephew Lot with his possessions and all the women and other captives.
Ya washe su da kuma dukan kayayyakinsu, ya kuma dawo da Lot danginsa da mallakarsa, tare da mata da sauran mutane.
After Abram returned from his victory over Kedorlaomer and all his allies, the king of Sodom went out to meet him in the valley of Shaveh (that is, the King’s Valley).
Bayan Abram ya dawo daga cin Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi a yaƙi, sai sarkin Sodom ya fito don yă tarye Abram a Kwarin Shabe (wato, Kwarin Sarki).
And Melchizedek, the king of Salem and a priest of God Most High, brought Abram some bread and wine.
Sai Melkizedek sarkin Salem ya kawo burodi da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Mafi Ɗaukaka,
Melchizedek blessed Abram with this blessing: “Blessed be Abram by God Most High, Creator of heaven and earth.
ya albarkaci Abram yana cewa, “Allah Mafi Ɗaukaka Mahaliccin sama da ƙasa yă albarkace Abram.
And blessed be God Most High, who has defeated your enemies for you.” Then Abram gave Melchizedek a tenth of all the goods he had recovered.
Kuma albarka ta tabbata ga Allah Mafi Ɗaukaka wanda ya ba da maƙiyanka a hannunka.” Sa’an nan Abram ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na kome.
The king of Sodom said to Abram, “Give back my people who were captured. But you may keep for yourself all the goods you have recovered.”
Sarkin Sodom ya ce wa Abram, “Ka ba ni mutanena da ka ƙwace daga hannun sarakunan nan kawai, ka riƙe kayayyakin don kanka.”
Abram replied to the king of Sodom, “I solemnly swear to the Lord , God Most High, Creator of heaven and earth,
Amma Abram ya ce, wa sarkin Sodom, “Na ɗaga hannu ga Ubangiji Allah Mafi Ɗaukaka, Mahaliccin sama da ƙasa, na riga na rantse
that I will not take so much as a single thread or sandal thong from what belongs to you. Otherwise you might say, ‘I am the one who made Abram rich.’
cewa ba zan karɓi kome da yake naka ba, ko zare ko maɗaurin takalma, don kada ka ce, ‘Na azurta Abram.’
I will accept only what my young warriors have already eaten, and I request that you give a fair share of the goods to my allies—Aner, Eshcol, and Mamre.”
Ba zan karɓi kome ba, sai dai abin da mutanena suka ci da kuma rabon mutanen da suka tafi tare da ni, ga Aner, Eshkol, da Mamre. Bari su ɗauki rabonsu.”
Some time later, the Lord spoke to Abram in a vision and said to him, “Do not be afraid, Abram, for I will protect you, and your reward will be great.”
Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
But Abram replied, “O Sovereign Lord , what good are all your blessings when I don’t even have a son? Since you’ve given me no children, Eliezer of Damascus, a servant in my household, will inherit all my wealth.
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
You have given me no descendants of my own, so one of my servants will be my heir.”
Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
Then the Lord said to him, “No, your servant will not be your heir, for you will have a son of your own who will be your heir.”
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
Then the Lord took Abram outside and said to him, “Look up into the sky and count the stars if you can. That’s how many descendants you will have!”
Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
And Abram believed the Lord , and the Lord counted him as righteous because of his faith.
Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
Then the Lord told him, “I am the Lord who brought you out of Ur of the Chaldeans to give you this land as your possession.”
Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
But Abram replied, “O Sovereign Lord , how can I be sure that I will actually possess it?”
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
The Lord told him, “Bring me a three-year-old heifer, a three-year-old female goat, a three-year-old ram, a turtledove, and a young pigeon.”
Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
So Abram presented all these to him and killed them. Then he cut each animal down the middle and laid the halves side by side; he did not, however, cut the birds in half.
Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
Some vultures swooped down to eat the carcasses, but Abram chased them away.
Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
As the sun was going down, Abram fell into a deep sleep, and a terrifying darkness came down over him.
Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
Then the Lord said to Abram, “You can be sure that your descendants will be strangers in a foreign land, where they will be oppressed as slaves for 400 years.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
But I will punish the nation that enslaves them, and in the end they will come away with great wealth.
Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
(As for you, you will die in peace and be buried at a ripe old age.)
Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
After four generations your descendants will return here to this land, for the sins of the Amorites do not yet warrant their destruction.”
A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
After the sun went down and darkness fell, Abram saw a smoking firepot and a flaming torch pass between the halves of the carcasses.
Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
So the Lord made a covenant with Abram that day and said, “I have given this land to your descendants, all the way from the border of Egypt to the great Euphrates River—
A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
the land now occupied by the Kenites, Kenizzites, Kadmonites,
ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
Hittites, Perizzites, Rephaites,
Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
Amorites, Canaanites, Girgashites, and Jebusites.”
Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”
Now Sarai, Abram’s wife, had not been able to bear children for him. But she had an Egyptian servant named Hagar.
To, Saira, matar Abram, ba tă haifa masa ’ya’ya ba. Amma tana da wata baiwa mutuniyar Masar mai suna Hagar,
So Sarai said to Abram, “The Lord has prevented me from having children. Go and sleep with my servant. Perhaps I can have children through her.” And Abram agreed with Sarai’s proposal.
saboda haka sai ta ce wa Abram, “ Ubangiji ya hana mini haihuwar ’ya’ya. Tafi ka kwana da baiwata; wataƙila in sami iyali ta wurinta.” Abram kuwa ya yarda da abin da Saira ta faɗa.
So Sarai, Abram’s wife, took Hagar the Egyptian servant and gave her to Abram as a wife. (This happened ten years after Abram had settled in the land of Canaan.)
Saboda haka bayan Abram ya yi zama a Kan’ana shekaru goma, Saira matarsa ta ɗauki Hagar baiwarta ta ba wa mijinta tă zama matarsa.
So Abram had sexual relations with Hagar, and she became pregnant. But when Hagar knew she was pregnant, she began to treat her mistress, Sarai, with contempt.
Abram kuwa ya kwana da Hagar, ta kuma yi ciki. Sa’ad da Hagar ta gane tana da ciki, sai ta fara rena uwargijiyarta.
Then Sarai said to Abram, “This is all your fault! I put my servant into your arms, but now that she’s pregnant she treats me with contempt. The Lord will show who’s wrong—you or me!”
Sai Saira ta ce wa Abram, “Kai ne da alhakin wahalan nan da nake sha. Na sa baiwata a hannunka, yanzu da ta sani tana da ciki, sai ta fara rena ni. Bari Ubangiji yă shari’anta tsakanina da kai.”
Abram replied, “Look, she is your servant, so deal with her as you see fit.” Then Sarai treated Hagar so harshly that she finally ran away.
Abram ya ce, “Baiwarki tana a hannunki? Ki yi da ita yadda kika ga ya fi kyau.” Sai Saira ta wulaƙanta Hagar; saboda haka ta gudu daga gare ta.
The angel of the Lord found Hagar beside a spring of water in the wilderness, along the road to Shur.
Mala’ikan Ubangiji ya sami Hagar kusa da maɓulɓula a jeji, ita ce maɓulɓular da take gefen hanya zuwa Shur.
The angel said to her, “Hagar, Sarai’s servant, where have you come from, and where are you going?” “I’m running away from my mistress, Sarai,” she replied.
Ya kuma ce mata, “Hagar, baiwar Saira, daga ina kika fito, kuma ina za ki?” Ta amsa ta ce, “Ina gudu ne daga wurin uwargijiyata Saira.”
The angel of the Lord said to her, “Return to your mistress, and submit to her authority.”
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce mata, “Koma wurin uwargijiyarki Saira, ki yi mata biyayya.”
Then he added, “I will give you more descendants than you can count.”
Mala’ikan ya ƙara da cewa, “Zan ƙara zuriyarki har su yi yawan da ba wanda zai iya lasafta su.”
And the angel also said, “You are now pregnant and will give birth to a son. You are to name him Ishmael (which means ‘God hears’), for the Lord has heard your cry of distress.
Mala’ikan Ubangiji ya kuma ce mata, “Ga shi kina da ciki za ki kuwa haifi ɗa. Za ki ba shi suna Ishmayel, gama Ubangiji ya ga wahalarki.
This son of yours will be a wild man, as untamed as a wild donkey! He will raise his fist against everyone, and everyone will be against him. Yes, he will live in open hostility against all his relatives.”
Zai zama mutum mai halin jakin jeji. Hannunsa zai yi gāba da kowa, hannun kowa kuma zai yi gāba da shi. Zai yi zama gāba ga dukan ’yan’uwansa.”
Thereafter, Hagar used another name to refer to the Lord , who had spoken to her. She said, “You are the God who sees me.” She also said, “Have I truly seen the One who sees me?”
Sai ta ba wa Ubangiji wanda ya yi magana da ita, wannan suna. “Kai Allah ne wanda yake ganina,” gama ta ce, “Yanzu na ga wanda yake ganina.”
So that well was named Beer-lahai-roi (which means “well of the Living One who sees me”). It can still be found between Kadesh and Bered.
Shi ya sa ake kira rijiyar Beyer-Lahai-Royi tana nan har yanzu, tsakanin Kadesh da Bered.
So Hagar gave Abram a son, and Abram named him Ishmael.
Haka fa Hagar ta haifa wa Abram ɗa, Abram kuwa ya ba da suna Ishmayel ga ɗan da ta haifa.
Abram was eighty-six years old when Ishmael was born.
Abram yana da shekaru 86 sa’ad da Hagar ta haifa masa Ishmayel.
When Abram was ninety-nine years old, the Lord appeared to him and said, “I am El-Shaddai—‘God Almighty.’ Serve me faithfully and live a blameless life.
Sa’ad da Abram ya yi shekaru 99, sai Ubangiji ya bayyana a gare shi ya ce, ni “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi tafiya a gabana ka kuma zama marar abin zargi.
I will make a covenant with you, by which I will guarantee to give you countless descendants.”
Zan tabbatar da alkawarina tsakanina da kai, zan kuma ƙara zuriyarka ta yi yawa.”
At this, Abram fell face down on the ground. Then God said to him,
Abram ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, Allah kuma ya ce masa,