0
stringlengths
3
620
1
stringlengths
4
423
Lamech’s other wife, Zillah, gave birth to a son named Tubal-cain. He became an expert in forging tools of bronze and iron. Tubal-cain had a sister named Naamah.
Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe. ’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
One day Lamech said to his wives, “Adah and Zillah, hear my voice; listen to me, you wives of Lamech. I have killed a man who attacked me, a young man who wounded me.
Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
If someone who kills Cain is punished seven times, then the one who kills me will be punished seventy-seven times!”
Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
Adam had sexual relations with his wife again, and she gave birth to another son. She named him Seth, for she said, “God has granted me another son in place of Abel, whom Cain killed.”
Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
When Seth grew up, he had a son and named him Enosh. At that time people first began to worship the Lord by name.
Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji .
This is the written account of the descendants of Adam. When God created human beings, he made them to be like himself.
Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Sa’ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
He created them male and female, and he blessed them and called them “human.”
Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Sa’ad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
When Adam was 130 years old, he became the father of a son who was just like him—in his very image. He named his son Seth.
Sa’ad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
After the birth of Seth, Adam lived another 800 years, and he had other sons and daughters.
Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata.
Adam lived 930 years, and then he died.
Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, sa’an nan ya mutu.
When Seth was 105 years old, he became the father of Enosh.
Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
After the birth of Enosh, Seth lived another 807 years, and he had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata.
Seth lived 912 years, and then he died.
Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, sa’an nan ya mutu.
When Enosh was 90 years old, he became the father of Kenan.
Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
After the birth of Kenan, Enosh lived another 815 years, and he had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata.
Enosh lived 905 years, and then he died.
Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu.
When Kenan was 70 years old, he became the father of Mahalalel.
Sa’ad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
After the birth of Mahalalel, Kenan lived another 840 years, and he had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata
Kenan lived 910 years, and then he died.
Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, sa’an nan ya mutu.
When Mahalalel was 65 years old, he became the father of Jared.
Sa’ad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
After the birth of Jared, Mahalalel lived another 830 years, and he had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata
Mahalalel lived 895 years, and then he died.
Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, sa’an nan ya mutu.
When Jared was 162 years old, he became the father of Enoch.
Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
After the birth of Enoch, Jared lived another 800 years, and he had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata.
Jared lived 962 years, and then he died.
Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, sa’an nan ya mutu.
When Enoch was 65 years old, he became the father of Methuselah.
Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
After the birth of Methuselah, Enoch lived in close fellowship with God for another 300 years, and he had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata.
Enoch lived 365 years,
Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365.
walking in close fellowship with God. Then one day he disappeared, because God took him.
Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
When Methuselah was 187 years old, he became the father of Lamech.
Sa’ad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
After the birth of Lamech, Methuselah lived another 782 years, and he had other sons and daughters.
Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata.
Methuselah lived 969 years, and then he died.
Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, sa’an nan ya mutu.
When Lamech was 182 years old, he became the father of a son.
Sa’ad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
Lamech named his son Noah, for he said, “May he bring us relief from our work and the painful labor of farming this ground that the Lord has cursed.”
Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana ta’aziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la’anta.”
After the birth of Noah, Lamech lived another 595 years, and he had other sons and daughters.
Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da ’ya’ya maza da mata.
Lamech lived 777 years, and then he died.
Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, sa’an nan ya mutu.
After Noah was 500 years old, he became the father of Shem, Ham, and Japheth.
Bayan Nuhu ya yi shekara 500, sai ya haifi Shem, Ham da Yafet.
Then the people began to multiply on the earth, and daughters were born to them.
Sa’ad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu ’ya’ya mata,
The sons of God saw the beautiful women and took any they wanted as their wives.
sai ’ya’yan Allah maza suka ga cewa ’ya’yan mutane mata suna da bansha’awa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
Then the Lord said, “My Spirit will not put up with humans for such a long time, for they are only mortal flesh. In the future, their normal lifespan will be no more than 120 years.”
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arba’in ne.”
In those days, and for some time after, giant Nephilites lived on the earth, for whenever the sons of God had intercourse with women, they gave birth to children who became the heroes and famous warriors of ancient times.
Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a sa’ad da ’ya’yan Allah suka kwana da ’ya’yan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu ’ya’ya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
The Lord observed the extent of human wickedness on the earth, and he saw that everything they thought or imagined was consistently and totally evil.
Ubangiji kuwa ya lura cewa muguntar mutum ta yi yawa a duniya, kuma kowane abin da yake tunani a zuciyarsa mugu ne kawai a kowanne lokaci.
So the Lord was sorry he had ever made them and put them on the earth. It broke his heart.
Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya zafe shi ƙwarai.
And the Lord said, “I will wipe this human race I have created from the face of the earth. Yes, and I will destroy every living thing—all the people, the large animals, the small animals that scurry along the ground, and even the birds of the sky. I am sorry I ever made them.”
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan kawar da mutum, da dabbobi, da halittu masu rarrafe a ƙasa da kuma tsuntsayen sama waɗanda na halitta, daga doron ƙasa, saboda na damu da na yi su.”
But Noah found favor with the Lord .
Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji .
This is the account of Noah and his family. Noah was a righteous man, the only blameless person living on earth at the time, and he walked in close fellowship with God.
Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
Noah was the father of three sons: Shem, Ham, and Japheth.
Nuhu yana da ’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
Now God saw that the earth had become corrupt and was filled with violence.
Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
God observed all this corruption in the world, for everyone on earth was corrupt.
Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
So God said to Noah, “I have decided to destroy all living creatures, for they have filled the earth with violence. Yes, I will wipe them all out along with the earth!
Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
“Build a large boat from cypress wood and waterproof it with tar, inside and out. Then construct decks and stalls throughout its interior.
Saboda haka ka yi wa kanka jirgi da katakon Saifires , ka yi ɗakuna a cikinsa, ka shafe shi da ƙaro ciki da waje.
Make the boat 450 feet long, 75 feet wide, and 45 feet high.
Ga yadda za ka gina shi; jirgin zai kasance mai tsawon ƙafa 45, fāɗinsa ƙafa 75, tsayinsa kuma ƙafa 45.
Leave an 18-inch opening below the roof all the way around the boat. Put the door on the side, and build three decks inside the boat—lower, middle, and upper.
Ka yi masa rufi, ka kuma ba da fili inci 18 tsakanin rufin a kowane gefen jirgin. Ka sa ƙofa a gefen jirgin. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe.
“Look! I am about to cover the earth with a flood that will destroy every living thing that breathes. Everything on earth will die.
Ga shi zan aiko da ambaliya ruwa a duniya, in hallaka dukan mai rai da yake a ƙarƙashin sama, kowace halittar da take numfashi a cikinta. Dukan abin da yake a duniya zai hallaka.
But I will confirm my covenant with you. So enter the boat—you and your wife and your sons and their wives.
Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da ’ya’yanka maza da matarka da matan ’ya’yanka tare da kai.
Bring a pair of every kind of animal—a male and a female—into the boat with you to keep them alive during the flood.
Za ka shigar da biyu na dukan halittu masu rai, namiji da ta mace a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai.
Pairs of every kind of bird, and every kind of animal, and every kind of small animal that scurries along the ground, will come to you to be kept alive.
Biyu na kowane irin tsuntsu, kowace irin dabba da kuma kowace irin halitta mai rarrafe a ƙasa, za su zo wurinka domin a bar su da rai.
And be sure to take on board enough food for your family and for all the animals.”
Za ka ɗauki kowane irin abinci wanda za a ci, ka adana don yă zama abincinka da nasu.”
So Noah did everything exactly as God had commanded him.
Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.
When everything was ready, the Lord said to Noah, “Go into the boat with all your family, for among all the people of the earth, I can see that you alone are righteous.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
Take with you seven pairs—male and female—of each animal I have approved for eating and for sacrifice, and take one pair of each of the others.
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
Also take seven pairs of every kind of bird. There must be a male and a female in each pair to ensure that all life will survive on the earth after the flood.
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
Seven days from now I will make the rains pour down on the earth. And it will rain for forty days and forty nights, until I have wiped from the earth all the living things I have created.”
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
So Noah did everything as the Lord commanded him.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
Noah was 600 years old when the flood covered the earth.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
He went on board the boat to escape the flood—he and his wife and his sons and their wives.
Nuhu da matarsa da ’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
With them were all the various kinds of animals—those approved for eating and for sacrifice and those that were not—along with all the birds and the small animals that scurry along the ground.
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
They entered the boat in pairs, male and female, just as God had commanded Noah.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
After seven days, the waters of the flood came and covered the earth.
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
When Noah was 600 years old, on the seventeenth day of the second month, all the underground waters erupted from the earth, and the rain fell in mighty torrents from the sky.
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
The rain continued to fall for forty days and forty nights.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
That very day Noah had gone into the boat with his wife and his sons—Shem, Ham, and Japheth—and their wives.
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da ’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
With them in the boat were pairs of every kind of animal—domestic and wild, large and small—along with birds of every kind.
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
Two by two they came into the boat, representing every living thing that breathes.
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
A male and female of each kind entered, just as God had commanded Noah. Then the Lord closed the door behind them.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
For forty days the floodwaters grew deeper, covering the ground and lifting the boat high above the earth.
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
As the waters rose higher and higher above the ground, the boat floated safely on the surface.
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
Finally, the water covered even the highest mountains on the earth,
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
rising more than twenty-two feet above the highest peaks.
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
All the living things on earth died—birds, domestic animals, wild animals, small animals that scurry along the ground, and all the people.
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
Everything that breathed and lived on dry land died.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
God wiped out every living thing on the earth—people, livestock, small animals that scurry along the ground, and the birds of the sky. All were destroyed. The only people who survived were Noah and those with him in the boat.
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
And the floodwaters covered the earth for 150 days.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.
But God remembered Noah and all the wild animals and livestock with him in the boat. He sent a wind to blow across the earth, and the floodwaters began to recede.
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
The underground waters stopped flowing, and the torrential rains from the sky were stopped.
Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
So the floodwaters gradually receded from the earth. After 150 days,
Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
exactly five months from the time the flood began, the boat came to rest on the mountains of Ararat.
A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
Two and a half months later, as the waters continued to go down, other mountain peaks became visible.
Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
After another forty days, Noah opened the window he had made in the boat
Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
and released a raven. The bird flew back and forth until the floodwaters on the earth had dried up.
ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
He also released a dove to see if the water had receded and it could find dry ground.
Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
But the dove could find no place to land because the water still covered the ground. So it returned to the boat, and Noah held out his hand and drew the dove back inside.
Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
After waiting another seven days, Noah released the dove again.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
This time the dove returned to him in the evening with a fresh olive leaf in its beak. Then Noah knew that the floodwaters were almost gone.
Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
He waited another seven days and then released the dove again. This time it did not come back.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
Noah was now 601 years old. On the first day of the new year, ten and a half months after the flood began, the floodwaters had almost dried up from the earth. Noah lifted back the covering of the boat and saw that the surface of the ground was drying.
A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
Two more months went by, and at last the earth was dry!
A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
Then God said to Noah,
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
“Leave the boat, all of you—you and your wife, and your sons and their wives.
“Fito daga jirgin, kai da matarka da ’ya’yanka maza da matansu.
Release all the animals—the birds, the livestock, and the small animals that scurry along the ground—so they can be fruitful and multiply throughout the earth.”
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”